GIRMAN KAI, RAWANIN TSIYA.........

Friday, 21 October 2016

Ra'ayi II N.U.T, SIYASA, RASHAWA DA TABARBAREWAR ILIMI A JIHAR KATSINA : Ina Mafita ? - Daga Yusuf Umar Dutsin-ma




A duk lokuttan da zaka zagaya makarantunmu, za kayi kacibus da matsaloli iri daban daban. Wadanda suka hada da rashin isassun Malamai, qarancin ababen zama da rubutu, sanyi-sanyi wajen gudanar da aiki daga 6angaren Malamai; da dai sauran matsaloli nan-da-can.

Da dama, mu kanyi tunani da tambayar ‘menene ummul-aba’isin’ wadannan matsaloli da Ilimin yake samu. A wannan kasida, munyi duba izuwa Kungiyar Malamai ta NU..T da Rashawa akan manya-manyan matsalolin da suke addabar huddatayyar Ilimi a Jihar Katsina.

Wednesday, 19 October 2016

Ra'ayi || An dade ana ruwa kasa na shanyewa : Daga Abdullahi Shehu Duniya. (Karanta)

Abdullahi Shehu

Lalatattun shugabanni, bare gurbin malamai tare da 'Yan boko akida sun dade suna gasa mana gyada a hannu.

- LALATATTUN SHUGABANNI sune suke rike da madafun iko a kasar nan shekara da shekaru ba tare da sun tsinanama kasar nan komai ba face kwashe dukiyar kasa da kuma jefa kasar cikin mawuyacin hali irin Wanda muke ciki a yau.
Su irin wadannan shugabanni basu amfanar kowa da komai face iyalansu da 'Yan 'uwan matansu, sai kuma mutane kalilan da suka san za suyi masu amfani wajen biyan bukatunsu na sharri.