A duk lokuttan da zaka zagaya
makarantunmu, za kayi kacibus da matsaloli iri daban daban. Wadanda suka hada
da rashin isassun Malamai, qarancin ababen zama da rubutu, sanyi-sanyi wajen
gudanar da aiki daga 6angaren Malamai; da dai sauran matsaloli nan-da-can.
Da dama, mu kanyi tunani da tambayar
‘menene ummul-aba’isin’ wadannan matsaloli da Ilimin yake samu. A wannan
kasida, munyi duba izuwa Kungiyar Malamai ta NU..T da Rashawa akan manya-manyan
matsalolin da suke addabar huddatayyar Ilimi a Jihar Katsina.

