GIRMAN KAI, RAWANIN TSIYA.........

Friday, 21 October 2016

Ra'ayi II N.U.T, SIYASA, RASHAWA DA TABARBAREWAR ILIMI A JIHAR KATSINA : Ina Mafita ? - Daga Yusuf Umar Dutsin-ma




A duk lokuttan da zaka zagaya makarantunmu, za kayi kacibus da matsaloli iri daban daban. Wadanda suka hada da rashin isassun Malamai, qarancin ababen zama da rubutu, sanyi-sanyi wajen gudanar da aiki daga 6angaren Malamai; da dai sauran matsaloli nan-da-can.

Da dama, mu kanyi tunani da tambayar ‘menene ummul-aba’isin’ wadannan matsaloli da Ilimin yake samu. A wannan kasida, munyi duba izuwa Kungiyar Malamai ta NU..T da Rashawa akan manya-manyan matsalolin da suke addabar huddatayyar Ilimi a Jihar Katsina.


KUNGIYAR N.U.T
Kungiyar N.U.T kamar yadda kowa ya sani, Kungiya ce wadda aka assasa ta don kare haqqin Malamai da Malumta a fadin Kasar Najeriya. Duk da cewar ta wani fannin suna dan yin qoqari; amma mafi yawanci tagomashin da Ilimi yake samu ya samo asali ne da irin yadda ake tafiyar da ita wannan Kungiya.

Zamu iya cewa, abinda Kungiyar N.U.T tafi qwarewa akan shi shine YAJIN AIKI (Strike); wanda koda sunyi shi ma ba wani da mai ido yake haifarwa ba. Sauran Kungiyoyi, alal misali na ma’aikatan lafiya; sunyi rawar gani a Jiha ta wajen kawo cigaba da walwala (welfare) ga ‘ya’yan su – kama daga Karin albashi, Karin girma, kudaden alawus-alawus da sauransu.

Amma abin takaici ga 6angaren Malamai shine, yadda ita wannan Kungiya take tatsar su (task) a kowane wata ba tare da kwalliya na biyan kudin sabulu ba. Kuma a aikace ba wani aikin da za’a iya nuna maka ace yau gashi N.U.T tayi shi.

A Jihar Katsina, irin salon Mulkin da N.U.T ke gudanarwa yana daya daga cikin abubuwan dake kawo cikas ga cigaban ilimi birni da kauye; kuma idan ba mataki aka dauka ba, to wannan matsalar zata ci gaba da kasancewa kenan har ranar da ba’a sani ba.

SIYASA
Wannan ma wata babbar matsala ce wadda take addabar cigaban Ilimi a Jihar Katsina, ta yadda ‘yan siyasa suke da fada-a-ji musamman idan aka zo daukar ma’aikata, inda zaka ga sai dan wane-da-wane ne kadai ke samun shiga. Ko kuma, wanene ka sani, ko wanene ya aiko ka? Wannan kuwa ya jaza daukar Malamai wadanda basu da qwarewa kuma basu san makamar aiki ba.

Idan har Gwamnati da ‘yan siyasa zasu dauke hannunsu ga maganar daukar ma’aikata, a barwa hukumomin da abin ya shafa; to na tabbatar za’a samu cigaba mafi inganci domin kuwa sai wanda ya cancanta ne kawai za’a baiwa dama.

Akwai makarantu da dama wadanda idan ka bincika zaka ga cewa akwai Malamai maza da mata wadanda basu zuwa wajen aiki, wasu koda sunzo to basu gudanar da aikin su, wasu kuwa idan har zaka ga yadda suke koyarwa to zaka iya zubar da hawaye domin tunanin yadda makomar ‘ya’yanmu da qannenmu zata kasance. Kuma baka iya cewa KANZIL saboda su irin wadannan Malamai Matan wasu ne, ko ‘ya’yan wasu, ko dangin wasu.

RASHAWA
Muhimmin abinda ya kashe Kungiyar N.U.T da Siyasar kasar mu shine Rashawa – Rashawa kuwa kowa yasan tana cin ayyuka ne kamar yadda iska ke tafiyar da ruwa.

A yanzu, zaka ga cewa idan mutum zai kai ‘ya’yanshi makaranta sai ya hada da bada cin hanci da rashawa domin a dauke su. Musamman idan yasan basu kai matakin daya kamata a dauke su din ba. Malamai a makaranta sun maida rashawa kamar ruwan sha, ta yadda zaka ga Malami/Malama suna fifita ‘ya’yan masu kudi ko sarauta fiye da ‘ya’yan talakkawa.

Ko wajen transfer ta Malamai zuwa wasu makarantu, hukumomi suna taka rawa wajen barbadawa rashawa taki, a inda zaka ga matar wane da wane ko ‘dan wane da wance an ajiye su acikin gari, su kuwa malamai marasa galihu an watsa su kauyuka sannan an bisu da binbinin dubiya (supervision).

Idan har bamu taru muka yiwa wannan tufkar hanci ba, to lalle zamuci gaba da kasancewa cikin bango-daya (square one) ba tare da mun samu cigaban daya kamata ba.

*****                              ******                                      *******
Muna buqatar muji ra’ayoyinku akan hanyoyin magance wadannan matsaloli.

Sharhi,
Yusuf Umar Dutsin-ma
08031178528



No comments: